Ta kaitaccen Tarihin Malam Sa'adu Zungur Dan Siyasa kuma dan Gwagwarmaya, Mawaki.
An Haifi Malam Sa'adu Zungur ne a watan Nuwamban Shekarar 1914 a cikin garin Bauchi Bayan yayi karatun Islamiyya dakuma na Sauran Littatattafan Addini Addinin Musulunci Malam Ya halarci Makarantar Kwaleji na yaba dake birnin Legas a Shekarar 1934 Ya mutu a Shekarar 1958 Marigayi malam Sa'adu Zungur Shine Mutum na Farko daya fara kafa Jam'iyyar Siyasa a fadin Arewacin Nigeria
Malam Sa'adu Zungur Yakasance Yana daya daga Cikin Shahararrun marubutan Adabin harshen hausa Yakuma kasance dan Siyasa a Lokutan baya.
Sa'adu Yasha gwagwarmaya wajen yaki da yadda Turawan mulkin mallaka Suka mulki Kasar Nigeria A Wancan Lokaci.
Sannan kuma yakasance mutum ne mai kaifin basira, Tunani, hazaka dakuma hangen nesa.
A Shekarar 1942 ne Yasake dawowa garin bauchi inda yaci gaba da harkar karantarwa.
Bayan gamayya dasuka yi dasu Malam Aminu kano da muhammed baba halla nayin gwagwarmaya da yadda ake mulki a yankin arewa a wancan zamanin, Malam sa'adu Zungur yakasance Sakataren Jam'iyyar NCNC a Shekarar 1948.
Malam Sa'adu Zungur yayi Rubuce Rubuce dadama a fannin Adabin hausa.
Wasu daga cikin littattafan daya Rubuta Wadanda sukafi Shahara Sunhada da.
1. Arewa jamhuriya ko mulukiya.
2. Maraba da Soja.
Yakuma Kasance Abun koyi dakuma kwaikwayo ga sauran marubuta adabin harshen hausa irinsu, Malam Abubakar ladan Zariya da sauran marubuta adabin hausa.
Yarasu a cikin garin Bauchi a Shekarar 1958 Allah Yajikansa da rahama Amin.
Allah ya jikansa da Rahama
ReplyDelete